Translate

Dawakin-Tofa

10 Ga Satumba, 2014.
DAWAKIN-TOFA: Siyasa ko Masifa?

Daga: Amir Abdulazeez

K
u yi m in  afuwa idan kalmar ‘masifa’ da na yi amfani da ita a wannan sharhi ta yi tsauri da yawa. Amma magana ta gaskiya,  da wahala a iya amfani da wata kalmar ba ita ba wajen kwatanta ko bayyana irin yanayin da masu juya akalar siyasar Dawakin-Tofa suka sanya ta a ciki.
Kimanin sati uku da suka gabata, wani bawan Allah da muka fara mu’amala da shi a shekarar bara ya tare ni a gidan wani ɗaurin aure. Bayan mun gaisa, sai ya bani haƙuri bisa ƙauracemin da ya yi na kwana biyu. Yace ya ƙauracemin  ne saboda dalili na siyasa, domin wai ya na tsoron kada waɗanda ya kira iyayen gidansa na siyasa a Jam’iyyar APC ta Dawakin-Tofa su gane ya na mu’amala da ni ko kuma mutane iri na, su saka ƙafar wando ɗaya da shi, wai tunda a cewarsa da ni da jaridar da na ke wallafawa, ana yi musu kallon masu adawa da Maigirma Mataimakin Gwamnan Jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje da kuma wasu masu juya akalar APC a Dawakin-Tofa.
Da farko dai na so na tsare shi sai ya bayyana min abin da ni na yi ko jaridar wanda ya ke nuna ana adawa da Gandujen ko kuma da su iyayen gidan nasa, to amma sai na ga hakan ɓata lokaci ne, ba lallai ne in samu wata gamsuwa ba. Kawai sai na yi masa godiya , muka yi sallama, muka rabu ina jin tausayinsa bisa wannan hali da aka saka shi  ko kuma ya saka kansa a ciki.
Bayan ‘yan kwanaki da faruwar wannan sai na haɗu da wani mai riƙe da muƙami a gwamnatin ƙaramar hukumar Dawakin-Tofa ya na bayyana wa wani abokinsa (shi ma wani shahararraen ɗan siyasa) cewar iyayen gidansa sun shaida masa cewar kada ya ƙara alaƙa da wannan abokin nasa, idan ba haka ba zai ji a jikinsa. Waɗannan mutane biyu abokai ne shekara da shekaru kuma tare suka yi makaranta amma duk da wannan, wai ba a tunanin cewar wata hulɗar daban za ta iya haɗasu wadda ba ta siyasa ba. Kai in ma hulɗar siyasa za su yi tare, to sai me? Wai yaushe siyasa ta koma gaba ne. Wanna masifa da me ta yi kama?
Kwanakin baya aka dinga yaɗa labari cewar Honarabul Kawu Sumaila, ɗan takarar Gwamnan Jihar Kano, ya kira dukkan shugabannin mazaɓu na Jam’iyyar APC na ƙananan hukumomi 44 na Jihar Kano, amma wai sai aka hana na Dawakin-Tofa zuwa. Abin haushi da kunya, na ƙananan hukumomi 43 sun je amma ban da na Dawakin-Tofa.  Wannan ko mun ƙi ko mun so, saƙon da muke isar wa da duniya shi ne har yanzu Dawakin-Tofa siyasar gaba, duhun kai da jahilci muke yi ko da kuwa hakan ba gaskiya ba ne. Shin suna tsammanin da haka za a taimaki takarar Gandujen? Yanzu idan Maigirma, Dakta Ganduje ya kira shugabannin Sumaila suka ƙi zuwa, mu ‘yan Dawakin-Tofa ya za mu ji a ranmu? Idan kuma Kawu Sumailan Allah Ya ba wa Gwamnan Kano, ya ake tunanin zai ɗauki ‘yan Dawakin-Tofa misali? A siyasance don kana son wani, ba za ka yi mu’amala da kowa ba kenan?
Ya kamata Maigirma Mataimakin Gwamna ya tsawatarwa waɗannan mutane masu kiran kansu muƙarrabansa ko kuma masu sawa da hanawa a jam’iyyar APC ta Dawakin-Tofa, waɗanda su ake zargi da aikata irin waɗannan abubuwa. Idan kuma da yawunsa da yardarsa suke yin hakan , to sai a yi mana bayani domin mu san yadda abin ya ke. Ita dai gaskiya matuƙar ɗaci ne da ita, kusan kowa ba ya so a faɗa masa ita, amma idan ya daure ya karɓe ta ya yi amfani da ita, sakamakon ta zai zamo masa mai zaƙi.
Akwai buƙatar mu tuna cewar, shi goyon baya da haɗin kan jama’a, ba a samunsa ta ƙarfi, ana samunsa  ne a siyasance ta hanyar kyautatawa da laluma. Ko’ina sai ɓatawa Ganduje suna a ke yi da sunan tallata shi, kuma wannan ba ƙaramar mummunar illa ba ce ga wanda ya ke neman Gwamnan Kano ba wai Gwamnan Dawakin-Tofa, kuma a shekarar 2015 ba wai 2019 ba. Idan har muka ga shiru ba a samu gyara ba ko kuma ba a tsawatar ba, to za mu ƙaddara cewar Maigirma Ganduje shi ya ba su izinin duk wannan abu da suke yi.
Shi jagoranci da ɗaukaka, Allah Ne Ya ke ba da su, don haka mun yarda waɗannan mutane tauraruwarsu ita ta ke haskawa kuma lokacinsu ne, kuma su ne jagorori. To amma ya kamata su yi amfani da wannan dama don su bar kyakkyawan tarihi ta hanyar kawo gyara da cigaba, amma ba su dinga kama-karya, son zuciya tare da haddasa gaba a tsakanin jama’a ba.
Haka kawai yanzu an ɗauko wani salo, idan ka na neman wani muƙami na siyasa, sai a ce wai ai ba ka son Ganduje don haka a yaƙe ka, ko kuma a ce Ganduje ba kai ya ke so ba, don haka wai aikin banza ka ke, da kai da banza duk ɗaya,  ba za ka ci ba. To ko an manta cewar Allah Shi ya ke bayar da mulki? Duk wanda ya ke kan wata dama a yanzu, akwai wanda ya kai shi idan ba Allah ba? To ya kamata a sani, Ganduje uba ne, kuma mu a tunanin mu matsayinsa ya wuce a ce wai ya na son wane ko bay a son wane. Ya kamata a ce kowa na sa ne, kai har wanda ma ba ɗan jam’iyyarsa ba.
Dawakin-Tofa ƙaramar hukuma ce mai ɗumbin tarihi da daraja ba ma a Jihar Kano ba, a’a har a Najeriya baki ɗaya. Ta na daga cikin ƙananan hukumomi ƙirƙirar farko a Najeriya baki ɗaya kuma ita uwa ce da ta haifo kuma ta raini wasu ƙananan hukumomi irin su Bagawai, Tofa da Rimin-Gado. Amma abin takaici, yanzu dariya su ke mana suna cewar muna ƙarƙashin siyasar mulkin-mallaka, siyasar rashin ‘yanci da tsoro da danniya.
Wannan ƙaramar hukuma ba mallakin wani ba ce, ta mu ce baki ɗaya kuma haƙƙin mu ne  mu haɗu tare mu ga cewar mun ciyar da ita gaba. Amma idan wani ko wasu suna ganin cewa Dawakin-Tofa mallakar su ce kuma za su tilastawa mutane ta ƙarfin tsiya su yi abin da suke so, to ba kansu farau ba, kuma sai mu ce mu su: ‘Allah Ya bada sa’a’, gas u ga ‘yan Dawakin-Tofar nan, ai kowa ya san inda ya ke masa ciwo.

Mallam Amir shi ne Mawallafin Jaridar Muryar Dawakin-Tofa kuma Co-ordinator na shirin Dawakin-Tofa Development Programme.




26th March, 2014.
NAZARI AKAN KATOƁARAR DA JAM’IYYAR APC TA KE TAFKAWA A DAWAKIN-TOFA

Daga: Amir Abdulazeez

Sau tari mutum shi ya kan yi wa kansa  mummunar illa ko dai yana sane da gangan ko kuma ba ya sane cikin jahilci. Domin kuwa duk abin da ka ke yi a kowanne lokaci ya na da gagarumin tasiri a kan duk abin da zai sameka a yanzu ko kuma a wasu shekaru masu zuwa.
Lokacin da masu ruwa da tsakin tsohuwar jam’iyyar PDP Kwankwasiyya suka dinga zagayawa mazaɓun ƙaramar hukumar Dawakin-tofa suna tara mutane tare da neman goyon bayansu ta hanyar bayyana musu irin zalunci da kama karyar da uwar jam’iyyarsu ta PDP ta ƙasa a wancan lokaci ta ke yi musu tare da jagororinsu, da yawa daga cikin jama’a sun ɗauka da gaske suke yi, gyara suke nema.
A lokacin wannan zagaye, al’ummar Dawakin-tofa sun kasu kashi uku. Kashin farko sun amince da maganganun waɗannan mutane saboda tsananin ƙiyayayrsu ga PDP a ƙarƙashin jagorancin Shugaban Ƙasa Goodluck Jonathan. Wasu kuma sun amince tare da amanna da su saboda ganin girma da darajar Gwamnan Kano Rabi’u Musa Kwankwaso da Mataimakinsa Dakta Abdullahi Ganduje.
Kashi na biyu sune wadanda kwata-kwata basu amince da maganganun waɗannan  mutane ba domin sun san dama ce kawai ta suɓuce daga hannunsu da kuma jagororinsu saboda lokacin da damar jagorancin PDP ɗin ya ke hannunsu ai ba a ji kansu ba. Domin haka a yanzu suna so su yi amfani da wannan dama don su yaudari mutane.
Kashi na uku sune wadanda suka tsaya a tsakiya, su basu gaskata ba, su basu ƙaryata ba, illa dai kawai sun zuba musu ido da zummar cewa lokaci shi zai nuna gaskiyar komai. Ga shi kuma lokacin ya fara nunawa.
Tun ba yau ba, ni ina ganin cewa mafi yawan ‘yan siyasa kusan duk halinsu ɗaya wato son zuciya da kuma kokarin kama karya ta hanyar ƙarfa-ƙarfa da handame dukkan wata dama. Don haka ina daga cikin wadanda suke da matuƙar shakku akan APC  tun daga sama har ƙasa. Kowa ya riga ya san ita PDP azzaluma ce gar da gar wani lokacin ma ko ɓoyewa ba ta yi, amma ita kuwa APC munafuka ce wacce ta ke nuna adalci a fili amma zalunci a ɓoye. Ko kuma ta yi adalci akan abu mara tasiri kamar jin ra’ayoyin mutane  misali amma kuma ta yi zalunci akan abu mai matuƙar tasiri kamar fidda ‘yan takara.
Duk da wannan tunani nawa, kullum addu’a na ke  yi, Allah SWT Ya sa kada ya zama gaskiya. Allah Ya sa APC ta bai wa wannan tunani nawa kunya ta hanyar yin gaskiya da adalci, amma kash! Hakan ba ta samu ba.
A karamar hukuma ta ta Dawakin-tofa, Kwankwasiyya ta karɓe ragamar jagorancin APC ta danne sauran jam’iyyu, kai ka ce ACN, CPC, ANPP su suka shigo suka samu Kwankwasiyyar a cikin APC  ba wai Kwankasiyyar ce ta shiga ta same su ba.
Jagorancin APC a hannun  Kwankwasiyya a Dawakin-tofa ba shi ne abin damuwa ba, domin dama a siyasa mai ƙarfi, mulki, kuɗi da jama’a ai shi ne da jagoranci. To amma kama karya mai kama da rainin hankali da ake yi a wajen fidda ‘yan takarkarin shugabancin karamar hukuma da kansiloli ita ce abar damuwa.
Abin sai ka ce wasan yara, wai an kafa an tsare, dole sai ‘yan Kwankwasiyya ne za su yi takarar kansiloli ko ana sonsu ko ba a sonsu. Kuma a cikin ‘yan Kwankwasiyyar ma sai shafaffu da mai. Wannan katoɓara ce ba ƙarama ba.
Tun farko da an san wannan tsarin za a yi, da ba sai an wahalar da mutane ta hanyar yaudararsu cewa su fito takara dimokraɗiyya da adalci za a yi ba. Ashe duk maganar adalci, haɗin kai, dimokradiyya, ci gaba da kyautatawa da suke yi ashe duk yaudara suke wa mutane?
Ita kuma jam’iyyar ANPP ta Dawakin-tofa wacce za ta ɗan iya taɓuka wani abu na gyara akan wannan lamari, ta samu kanta a ƙarƙashin jagorancin mutane marasa kishi wadanda buƙatar kansu ce kawai a gabansu.
Idan kana takarar kansila, dole sai an sa ka ka janye ta ƙarfin tsiya ko baka so ta hanyar baka tsoro da yi maka barazana. Idan kuma ka ƙi sai a shirya wani haramtaccen zaɓe a kada kai. Shin kundin tsarin mulkin jam’iyyar APC ba ‘yar tinƙe yace a yi ba ne idan sulhu bai yiwu ba?
Masu yin wannan kama karya su tuna cewa fa kafin su, dubannan mutane sun samu wannan dama kuma yau ba ta hannun su sannan bayansu kuma damar za ta koma hannun wasu. Su tuna kama karyar da ANPP ta yi a zaɓen kananan hukumomi na 2007, yau ina ANPP? Ta tarwatse kuma ta wulaƙanta. Itama PDP duk wannan zaluncin da ta ke yi a Najeriya, za ta tarwatse a kan idonmu inshaAllah, domin Allah ba Ya barin masu kama karya, sai dai ya jinkirta musu kawai. Suma ANPP ɗin yana sonsu da shiriya shi ya sa ya koya musu hankali tun da wuri.
Na san ‘yan Kwankwasiyya suna ganin za su ci zaɓe ko ana so ko ba a so. Wannan gaskiya ne, to amma su tuna mai zai je ya zo, ba wai yanzu ba, a’a watarana.
Ya kamata wannan katoɓarar da APC take yi a Dawakin-tofa da sauran kananan hukumomin Jihar Kano su daina. Idan kuma ba za su iya dainawa ba to su rage domin aƙalla abin ya ɗan dace da hankali domin yanzu abin ya yi muni da yawa.
Allah ya kyauta.



19/11/2013
Nazari Akan Alƙiblar Siyasar Dawakin-Tofa Idan Kwankwaso Ya Koma APC


Daga: Amir Abdulazeez

Siyasa mai abin mamaki da kuma abin dariya. A siyasa ne, sai ka gama kushe mutum ciki da bayansa saboda bambancin ra’ayi sai kuma ku wayi gari a jam’iyya ɗaya kuma akan manufa ɗaya tare kuma da neman makoma iri ɗaya. Wani lokacin kuma sai ka gama yin Allah wadai da wata jam’iyya, sai ka samu kanka tsamo-tsamo a cikinta.
Idan banda haka, da Janaral Muhammadu Buhari ba za su zauna jam’iyya ɗaya da Cif Bisi Akande, shugaban riƙo na APC na ƙasa ba domin kuwa lokacin da Buhari ya yi juyin mulki, Bisi Akande shine Mataimakin Gwamna Bola Ige na Jihar Oyo kuma Buhari ya yanke musu ɗaurin shekaru barkatai a kurkuku dukkansu su biyun, amma yanzu gasu nan ba mai jin kansu. Yau ga Mallam Nuhu Ribadu a teburi ɗaya da mafi yawan mutanen da ya kira ɓarayi kuma maciya amana lakoacin da yake shugaban hukumar EFCC. Gashi yau babu amintattu masu gaskiya a gunsa kamarsu saboda jam’iyyarsu ɗaya..
Anan Kano ga Mallam Ibrahim Shekarau ya sake haɗewa da tsofaffin mataimakansa, Injiniya Magaji Abdullahi da kuma Injiniya Abdullahi Tijjani Gwarzo waɗanda suka rabu baran-baran, kuma mai yiwuwa nan da wasu ‘yan kwananki zai haɗe da babban kishiyarsa wato Dakta Rabi’u Musa Kwankwaso a cikin tafiya guda.
Dukkan alamu tun daga sama har ƙasa sun nuna cewa, Gwamna Rabi’u Musa Kwankwaso yana kan hanyarsa ta shigowa jam’iyyar APC. Koda yake ba za mu iya tantacewar ko za su shigo ne gabaɗaya tare da sauran ‘yan uwansa gwamnoni waɗanka aka fi sani da ‘yan 7 ko G-7, ko kuma shi kaɗai zai shigo ba. Amma babu shakka shigowarsa APC a yanzu zai canja al’amuran siyasa a Jihar Kano, wataƙila ma har da Najeriya baki ɗaya.
Anan Dawakin-Tofa, wani babban jigo a jam’iyyar PDP wanda bai bamu izinin bayyana sunansa ba ya tabbatar mana da cewa jam’iyyar tana kiran taro a kowacce mazaɓa don jin ra’ayin ‘ya’yanta, kuma kawo yanzu dukkan mazaɓun da suka ziyarta sun jaddada goyon bayansu ga Maigirma Gwamna kuma umarninsa kawai suke jira. Duk da cewa bai bayyana mana mazaɓun da aka gudanar da wannan taro ba, amma Muryar Dawakin-Tofa ta halarci taron da aka gudanar a mazaɓun Dawanau da Ƙwa, kuma tana sane da lokacin da aka gudanar da taron a mazaɓar Tumfafi, bugu da ƙari kuma ta san lokacin da ake shirye-shiryen gudanar da wannan taro a mazaɓun Dawakin-Tofa ta Gabas da Dawakin-Tofa ta Yamma.
To, ko ma dai da irin wannan taruka ko babu, dukkan mai bibiya ko nazari akan al’amuran siyasar PDP Kwankwasiyya, ya san cewa tafiya ce da aka gina ta akan umarni da kuma biyayya, wannan ce ma ta sa mutane da yawa za su yi mamakin yin taron jin ra’ayin jama’a saɓanin yadda aka saba a baya na a yanke hukunci sannan a turo umarni daga sama zuwa ƙasa. Wannan ya nuna jan ƙafa da kuma ɗar-ɗar ɗin da shi kansa Gwamna Kwankwaso yake yi kafin shigarsa APC ɗin.
Duk da cewa akwai tsirarun ‘yan Kwankwasiyya anan Jihar Kano da ake sa ran ba lallai su bi Kwankwaso zuwa APC ba, to amma da wahala a samu irinsu a nan Dawakin-Tofa. Koda yake a ‘yan kwanakinnan raɗe-raɗe sun cika gari cewa Mataimakin Gwamna, Dakta Abdullahi Umar Ganduje ba zai bi Kwankwaso izuwa wata sabuwar jam’iyya ba, amma kuma makusantansa sun fito sun ƙaryata wannan jita-jitar ta hanyar sanarwa a kafafen yaɗa labarai cewa Ganduje yana tare da Kwankwaso ɗari bisa ɗari komai ruwa komai iska.
Shi kansa Sakataren Yaɗa Labaran Ofishin Mataimakin Gwamnan, Bala Salihu Dawakin-Kudu da muka tuntuɓe shi, ya yi watsi da jita-jitar a matsayin aikin ‘yan adawa.To tunda ‘yan PDP Kwankwasiyya na Dawakin-Tofa, babu wanda suka sani banda Ganduje, to da wahala wani ya bijire.
Wani bincike da muka gudanar, ya nuna cewa, wasu daga cikin ‘yan Kwankwasiyya a Dawakin-Tofa za su bi Kwankwaso izuwa APC ne saboda basu da wani zaɓi amma ba don suna so ba saboda sun riga sun ɓata da kowa, kuma sun yi watsi da duk wani ɗan siyasa sun riƙe Kwankwaso da Ganduje. Don haka basu da kowa sai su, to kuma yanzu an kawo gaɓar da ba za su iya sauya iyayen gida ba. Wasu kuma za su bi ne saboda suna morar gwamnatin kuma ba za su so su rabu da mulkin ba.
Wani babban jigo a PDP wanda sha’anin komawarsa APC yake da ‘yar sarƙaƙiya da kuma rikitarwa shine Ɗan Majalisar Dokokin Jihar Kano Mai Wakiltar Ƙaramar Hukumar Dawakin-Tofa, Honarabul Saleh Ahmed Marke domin shi akwai tanadin doka a cikin tsarin mulkin Najeriya wacce ta tanadi cewa duk wani ɗan majalisa ba zai iya sauya jam’iyya ba sai ya yi asarar kujerarsa, koda yake zai iya fakewa da cewa ai jam’iyyar tasa ta rabe gida biyu. Amma idan aka yi la’akari da ƙarfin nufi da kuma zafin kishi irin na ɓangaren tsohuwar PDP ƙarkashin Alhaji Bamanga Tukur wacce ta yi barazanar tabbatar da cewa dukkan wani ɗan majalisa ɗan sabuwar PDP da ya bar PDP, to ya rasa kujerarsa. Kuma dolene a ɗauki wannan barazana da matuƙar muhimmanci, duba da cewa shugaban ƙasa a ɓangarensu yake banda kuma kotuna da lauyoyi da suke dasu.
Idan muka kalli jiga-jigan da suke cikin PDP da waɗanda suke cikin APC a Dawakin-Tofa, sai mu tambayi kanmu: wai shin idan suka cakuɗe waje guda, siyasar ma zata yiwu kuwa? Gashi dama dukkan manyan Dawakin-Tofa basa wuce wannan jam’iyyun guda biyu tun daga 1999. Ko shakka babu girma da muhimmancin wasu dole ya ragu saboda tsananin gasa da takara da za’a samu. Wata tambayar ita ce: shin za’a samu sauran wata jam’iyyar adawa kuwa? Babu mamaki ƙanana da sababbin jam’iyyu irinsu PDM da LABOUR PARTY su yi amfani da wannan dama su kawo kansu Dawakin-Tofa kuma mai yiwuwa su samu tarin magoya baya. Bayan haka, kada a manta da cewa akwai ‘yan tsohuwar PDP a Dawakin-Tofa waɗanda ba ‘yan Kwankwasiyya ba kuma suna nan za su yi zamansu daram a PDP tare da samun isasshiyar iskar shaƙa da sararin watayawa. Banda haka, za su samu dukkan goyon baya da gudunmawar da suke buƙata tun daga Abuja har zuwa kan Hassan Kafayos banda kuma Biloniya Muhammad Abacha wanda a shirye yake ya taimakesu. Duk da cewa ba’a san wanda zai jagoranci waɗannan mutane ba, to amma akwai Dakta Mahmood Baffa Yola, Babban Kwamishina a Jihar Kano na Hukumar Karɓar Ƙorafe-Ƙorafen Jama’a ta Tarayya. To amma wani hanzari ba gudu ba shine, kowa ya san kusancin Dakta Mahmood da Sanata Bello Hayatu Gwarzo wanda ana ganin duk inda za su a siyasance, tare za su je. Shi Maigirma Sanata, a farkon wannan rigima, an rawaito shi a cikin sanatoci 22 na sabuwar PDP amma kuma yanzu alamu sun nuna ya yi baya-baya duk da cewa yana da kyakkyawar alaƙa da Kwankwaso tun ba yau ba. Don haka ba za’a iya sanin inda Dakta Mahmood ya nufa ba sai an tantance makomar Sanata. To amma wani abin dubawa anan shine, idan har ‘yan tsohuwar PDP suka samu Dakta Mahmood Baffa Yola a matsayin jagora, to akwai yiwuwar su yi babban tasiri kasancewar mutane da yawa na yi masa kallon dattijon arziki wanda yake iya riƙe mutane.
Yanzu haka kuma guna-guni ya yawaita a cikin ‘yan APC ɗin da basa maraba da shigowar Gwamna Kwankwaso da Ganduje cewar, a ranar da suka shigo APC, su kuma kashegari za su sauya sheƙa zuwa PDP. Ko wannan barazana tasu gaske ce ko kuma kuri ce? Lokaci shi zai yi alƙalanci. Rahotanni sun nuna cewa su ‘yan tsohuwar PDP waɗanda aka yiwa laƙabi da ‘yan Garkuwa har sun fara shirye-shiryen kafa shugabancin riƙo na jam’iyyar a nan Dawakin-Tofa, wasu ma sun tabbatar da cewa an kafa wannan shugabanci ta ƙarƙashin kasa.
Ita kanta sabuwar amaryar wato APC, masana suna ganinta da tarin matsaloli iri-iri anan Dawakin-Tofa. A bayyane yake a fili cewa ‘yan tsohuwar ANPP sun riga sun kankane jam’iyyar tun kafin a je ko’ina kuma a shirye suke da su kafa shugabancinta ko da kuwa babu haɗin kan CPC da ACN. Abinda kawai zai hanasu cimma burinsu shine Injiniya Magaji Abdullahi wanda shine turken CPC. To amma idan aka yi la’akari da cewa kusan dukkan mutanen CPC da ANPP ɗin duk mabiyansa ne na da da na yanzu, ba lallai ne ya damu da waɗanda za su zama shugabanni ba. Ita kanta tsohuwar CPC ɗin ta Dawakin-Tofa, wani tsagi nata ana kyautata zaton ya bi Sanata Rufa’i Sani Hanga zuwa Jam’iyyar PDM. Rigimar da ta fatattaka ANPP zuwa CPC da ACN babu tabbacin ta warware, me yiwuwa ta ciki na ciki. To amma idan aka yi la’akari da aiki ba dare ba rana da wata ƙungiya mai rajin tabbatar da adalci da dimokraɗiyya a APC take yi, sai mu iya cewa za’a samu gyara. Wannan ƙungiya ta haɗa jiga-jigan tsofaffin ANPP, CPC da ACN ɗin. To amma matsalar shine, har yanzu da alamun cewa jiga-jigan tsohuwar ANPP basu yi amanna da wannan ƙungiya ba.
Wannan shine halin da APC take a yanzu, to yaya kuma a ce PDP Kwankwasiyya ta antayo cikinta?
Wani mutum da zai iya yin gagurumin tasiri a wannan rintsi shine, Ɗan Majalisar Tarayya Mai Wakiltar Dawakin-Tofa, Tofa da Rimin-Gado, Honarabul Tijjani Abdulkadir Joɓe domin kuwa ko ba komai a shekaru shida da ya shafe akan mulki, ya kafa sansani mai ƙarfi nasa na kansa anan Dawakin-Tofa wanda tunɓuke shi ko hanashi tasiri zai yi wahala. Kuma a matsayinsa na wanda yake riƙe da mulki, ko da ‘yan Kwankwasiyya sun shigo ba dolene su yi masa wani mummunan rauni ba musamman idan bai nuna zai yaƙesu ba. 
A yanzu bata fito fili akan wanene yake jagorantar jam’iyyar APC a Dawakin-Tofa ba tsakanin Injiniya Magaji Abdullahi da Dakta Maikano Rabi’u ba, balle kuma a ce ga Dakta Ganduje ya shigo. Gefe ɗaya kuma akwai jiga-jigai irinsu Mallam Alhassan Dawaki, Honarabul Saleh Shehu Kwuidawa da sauransu waɗanda har yanzu ba’a ji ƙwaƙƙwaran motsinsu ba. Ko kuma dan ba’a buga gangar siyasar ba ne?
A ƙarshe dole mu bar wa lokaci damarsa domin shi ne zai warware mana dukkan wannan ƙulle-ƙulle amma babu shakka za mu sha kallo nan ba da daɗewa ba domin kuwa koda Kwankwaso bai shigo APC ba to akwai yiwuwar ya bar PDP.


Matsalolin Ƙaramar Hukumar Dawakin-Tofa: Surutu Ba Zai Kaimu Ko’ina Ba

7th November, 2013
Daga: Amir Abdulazeez

“Na duba dukkan abokai amma ban samu abokin da ya fi kiyaye harshe ba.”
- Umar Ibn Al-Khattab (RA)

N
i a ganina, surutu iri uku ne; akwai surutu mai ma’ana kuma mai amfani, akwai surutu mai ma’ana amma mara amfani sannan akwai surutu mara ma’ana kuma mara amfani. Kowanne ɗaya daga cikin waɗannan nau’ika na surutu, akwai yanayi da muhallin da suka dace da shi.
Surutu mai ma’ana kuma mai amfani shine mutum ya yi magana akan abin da ya dace kuma a inda ya dace ko da kuwa zai kwana yana magana. Misali, idan za ka yi magana akan matsalar ilimi a ƙaramar hukumar Dawakin-Tofa, to ka tabbatar cewa kai masanin ilimi ne, in kuma ba haka ba, to ka tabbatar ka yi bincike kuma ka fahimci abin da ka ke magana akansa. Bayan haka sai ka nufi gurin waɗanda abin ya shafa kamar ofishin ma’aikatar ilimi misali sai ka baje kolinka a can. Ka ga anan kowa ya san surutunka na a kawo gyara ne.
Surutu mai ma’ana amma kuma mara amfani shine mutum ya yi magana akan abin da ya dace amma ba a inda ya dace ba. Misali shine, za ka yi magana akan matsalolin asibitin Dawakin-Tofa, sai aka yi sa’a ka yi cikakken bincike ka san matsalolin asibitin ciki da bai kuma kana da isassun hujjoji amma kuma sai aka wayi gari ka je gaban teburin mai shayi kana baje kolinka. To anan kaima da kanka, ka san ba gyara kake nema ba.
Shi kuwa surutu mara ma’ana kuma mara amfani bai kamata ma ya samu muhalli a gurin da aka san ciwon kai ba. Domin kuwa shine surutun da mutum zai dinga yin magana akan abin da bai sani ba ko bai fahimta ba kuma ya ƙi ya yi bincike akaisannan kuma ya dinga yin wannan surutun a gurin da bai dace ba. Idan da ma zai yi shi a gurin da ya dace, da sai a samu masu yi masa gyara ko tsokaci. Wani lokaci kuma mai irin wannan surutan, idan ka yi masa gyara to sai cibi ya zama ƙari. Irin waɗannan surutan ne wasu daga cikinmu suke yi a majalisu, guraren hira da kuma dandalin sada zumunta na facebook da sauran waɗansu kafafe. Wataƙila suna sane, ƙila kuma basu sani ba.
Shi dai surutu ko da akan alkhairi ne, idan ya yi yawa to ya kan zama illa ba ƙarama ba ga mai yinsa, balle kuma a ce akan sharri ake yawan yinsa.
Sanin kowa ne cewa mun wayi gari a ƙaramar hukumar Dawakin-Tofa, babu abin da muke yi sai kushe ƙaramar hukumarmu, ba babba ba yaro. Abin haushinma shine har da waɗanda basu ma cancanta su ce uffan ba idan ana maganar ƙaramar hukumar domin kuwa babu wata gudunmawa da suka taɓa bata, suma sun samu dama har kusheta suke yi. Bayan haka kuma gamu da kushe masu riƙe da madafan iko, na da da na yanzu da kuma sauran manyan mutane. To ba laifi don ka faɗakar da wanda yake da dama a hannunsa kuma bai yi amfani da ita ba don kawo cigaba, amma kafin ka yi hakan sai ka yi tunanin kaima damar da take hannunka komai ƙanƙartarta, amfanin me ka yi da ita domin cigaban ƙaramar hukumarka? Kuɗi da mulki ba sune kaɗai dama ba, lafiya, lokaci, ilimi, sana’a duk suma damammaki ne.
Ni na san cewa Dawakin-Tofa ta samu cigaba ta fannoni da yawa amma ba ma gani. Idan muka ɗauki misali a ɓangaren ilimi; kafin shekarar 2003, na san garuruwa da ƙauyuka da yawa a ƙaramar hukumar Dawakin-Tofa waɗanda basu da ko mutum ɗaya wanda ya gama makarantar gaba da sakandire walau a matakin Digiri, Diploma ko NCE. Ba zan faɗi sunan garuruwan ba amma a yanzu da wahala ka samu garin da za’a ce babu mai Digiri, Diploma ko NCE ko mutum ɗaya komai ƙauyancin garin. Wannan cigaba ne kuma dama shi cigaba ai da sikeli ake amfani ba wai da surutu ba. Aunawa ake yi a ga me kake da shi da kuma me kake da shi yanzu?
Na sani cewa, akwai ƙananan hukumomi da yawa da suka sha gabanmu a wasu fannoni na rayuwa amma mu ma mun sha gaban wasu ƙananan hukumomin a wasu fannonin. Misali, idan kace Bichi ta sha gabanmu ta fuskar ilimin boko, to ƙila mu kuma mun sha gabansu ta fuskar Ilimin Addini ko kuma ta fuskar noma.
Idan kuma burin wannan surutai namu shine mu wayi gari mun sha gaban kowacce ƙaramar hukuma a Jihar Kano ta kowanne fanni na rayuwa, to abin mai sauƙi ne, ba na tashin hankali ba ne. Abin da za mu yi shine, wannan buhunnan surutan namu, mu zazzage su mu ɗure su da aiki tuƙuru. Mu daina nunawa kowa yatsa, mu bazama, kowa a fanninsa ya dage ya ga ya kawo wani cigaba a karan kansa. Ya yi ta aiki ba ƙaƙƙautawa, inda ya gaji ko ya tsaya ko ya kasa, to sai wani ya ɗora har sai mun cimma burinmu.

Idan kuma muna ganin ba zamu iya haƙura da surutun ba, to ga wata shawara. Mu zaɓi wasu ɗaiɗaiku daga cikinmu mu ɗora musu alhakin shirya mana taron tattaunawa ko muhawara duk wata ko duk bayan wata uku a dinga zama a mazaɓa ɗaya ko a mazaɓu daban-daban, kowa yana faɗar albarkacin bakinsa kamar yadda aka yi a taron farfado da ilimi a kwanakin baya. Duk da dai cewa har yanzu taron farfaɗo da ilimin bai fara kawo wani sakamako a aikace ba amma ko ba komai an yi muhawara a ranar taron. Amma idan za’a yi irin wannan taro, sai a yi abin a natse kuma a hankalce tare da tattauna yadda za’a shawo kan matsalolinmu a aikace maimakon soki burutsu. Amma idan ba haka ba to irin wannan surutun ba zai kaimu ko’ina ba. 

No comments:

Post a Comment